Najeriya tayi Canjaras a wasanta na farko a gasar cin kofin Nahiyar Afirka
Najeriya ta fara wasanta na farko a gasar cin kofin Nahiyar Afirka dayin kunnen doki a wasan data buga da kasar Equatorial Guinea a birnin Abidjan na kasar Code ivore.
Dan wasan tsakiya na Equatorial Guinea Ivan Edu shine yafara sanya kasarsa agaba a mintuna na 36 kafin daga bisani a mintuna na 37 dan wasan gaba na Najeriya Victor Osimhen yawarware kwallon.
Victor Osimhen dai ya zubar da damarmaki da dama a wasan wanda yakamata ace Najeriyar ta lashe wasan.
Najeriya dai na fatan sake lashe wasan a karo na hudu bayanda ta lashe gasar karshe a shekarar 2013.